Connect with us

Ƙetare

Majalisar ɗinkin duniya ta buƙaci a gaggauta tsagaita wuta a Gaza

Published

on

Babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres, ya bukaci  da a gaggauta tsagaita wuta a Gaza, bayan da Isra’aila ta ce ta fara kai farmaki domin ƙwace birnin Gaza.

Guterres, ya ce, ya na da matuƙar muhimmanci a kiyaye da kashe-kashe da kuma lalata duƙiyar da wannan farmaki zai haddasa.

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar da fara kai matakin farko na farmakin a Gaza, inda firaiministan ƙasar Benjamin Netanyahu ya ce yunkuri ne na ganin ya ƙwace abin da ya kira waje na karshe a Gaza.

Jami’ai a Gaza sun ce dubban Falasɗinawa na tserewa birnin wanda Mutane fiye da miliyan guda ke rayuwa a cikinsa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!