Connect with us

Labarai

Majalisar Dattawa a Najeriya ta amince da sababbin hafsoshin tsaron kasar

Published

on

Majalisar Dattawa a  Najeriya ta amince da sababbin hafsoshin tsaron da Shugaba Bola Ahmad Tinubu  ya naɗa ranar Juma’a da ta gabata, bayan sauke tsaffin hafsoshin.

Majalisar dai ta amince da Laftanar Janar Olufemi Oluyede a matsayin babban hafsan tsaro, da kuma Manjo Janar Waidi Sha’ibu a matsayin hafsan sojan ƙasa, sai Rear Admiral Idi Abbas hafsan sojan ruwa, da kuma Air Marshall Kennedy Aneke hafsan sojan sama.

Yayin tantancewar da aka yi musu a yau Laraba, sabbin shugabannin sojan sun amsa wasu tambayoyi daga ‘yanmajalisar bayan gabatar da kan su da tarihin ayyukan da suka gudanar kafin naɗin nasu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!