Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar Dattawa ta bukaci gwamnatin tarayya ta binciko mayakan Boko-haram da suka tsere daga dajin Sambisa

Published

on

Majalisar Dattawa ta bukaci gwamnatin tarayya da ta binciki ko mayakan Boko-haram da suka tsere daga dajin Sambisa da kuma mayaka da suka tsere daga kasar Libya na da hannu cikin kashe-kashen da ke faruwa tsakanin makiyaya da manoma a jihar Benue.

Shugaban kwamitin kula da harkokin ‘yan-sanda na majalisar Sanata Abu Ibrahim ne ya yi wannan kiran yayin zantawar sa da manema labarai a Abuja.

Ya ce gudanar da bincike kan lamarin ya zama wajibi sakamakon irin muggan makamai da maharan ke amfani da su wanda ya ce a iya saninsu Fulani makiyaya basa amfani da bingigogi kirar AK47.

Sanata Abu Ibrahim ya ce bako shakka yakamata a binciki wannan lamarin, domin akwai kanshin gaskiya wajen zargin cewa mayakan Boko-Haram da sojoji da suka tsere daga kasar Libya na da hannu cikin kashe-kashen.

Ya kuma ce wajibi ne sufeto Janar na ‘yan-sanda Ibrahim Idris da sauran jami’an tsaro su fadada komar bincikensu domin gano gaskiyar wadanda ke da hannu cikin kashe-kashen.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!