Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar yan sanda ta sallami jami’anta uku bisa laifin barnatar da harsashi ba bisa ka’ida ba

Published

on

Rundunar yan sandan jihar Lagos ta kori wasu yansanda uku, biyu masu mukamin Sergent da kuma kofur guda daya bisa laifin barnatar da harsashi ba bisa ka’ida ba.

Yan sandan sun hadar da Sajan Saturday Osaseri da kuma sajan Segun Okun sai kuma kofur Adekunle Oluwarotimi bayan gurfanar da su gaban kwamitin da’a na rundunar yan sandan inda kwamitin ya ce yan sandan sun karya tsarin rundunar yan sandan.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan da ke Lagos SP Chike Oti ya ce wadanda ake zargi da aikata laifin sun aikata laifin ne a ranar 11 ga watan Janairu da misalin karfe 9 da rabi na dare a kan titin Amukoko.

Oti ya ce yadda yan sandan sukayi harbi da bindigogin su akan wasu matasa da ke zargin sun jefe su da duwatsu da rabar ruwa ya saba ka’ida.

Ya ce hakan ya sanya guda daga cikin matasan ya rasa ransa inda wasu da dama suka samu raunuka da dama.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!