Connect with us

Labarai

Majalisar Dattawa ta Dakatar da muhawarar gyaran dokar zaɓe

Published

on

Majalisar Dattawan kasar nan ta dakatar da muhawarar gyaran Dokar Zaɓe, inda ta yanke shawarar shiga tattaunawar sirri a bayan fage  kafin ɗaukar matsaya ta ƙarshe.

 

Shugabannin Majalisar sun bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne domin bai wa ‘yan majalisar damar nazari mai zurfi kan ƙudirin gyaran dokar, tare da tattaunawa a tsakaninsu ba tare da matsin lamba ba.

 

A cewar Majalisar, manufar dakatar da muhawarar ita ce kauce wa yin gaggawa wajen yanke hukunci kan dokar da ke da matuƙar muhimmanci ga tsarin dimokuraɗiyyar ƙasar nan, musamman yadda za ta shafi zaɓe da sahihancinsu.

 

Majalisar ta ce za ta dawo kan batun ne bayan kammala tattaunawar sirrin da kuma samun fahimta ɗaya a kan muhimman sassa na gyaran dokar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!