Labarai
Majalisar Dattawa ta fara gyaran kundin tsarin mulkin kasa na 1999

Majalisar Dattawa ta kasa ta fara daukar matakan gyara kundin tsarin mulki na shekarar 1999 domin kara kaso na kudaden shiga da Gwamnatin Tarayya ke samu daga Asusun Tarayyar. Majalisar ta ce tsarin rabon kudaden da ake amfani da shi a yanzu bai dace da yawan nauyin al’umma da ke kan gwamnatin ba, musamman a fannin tsaro da sauran ayyukan more rayuwa.
Gwamnatin Tarayya dai na karbar kashi 52.68, yayin da jihohi 36 ke karbar kashi 26.72, sannan kananan hukumomi 774 ke samun kashi 20.60 na kudaden shiga.
Duk da haka, kudirin da Sanata Sunday Karimi na Kogi ta Yamma ya gabatar ya nemi a kara wa Gwamnatin Tarayya kaso, yana mai cewa tsarin da ake da shi ya tsufa kuma ba ya iya daukar nauyin ayyukan kasa.
Sanata Karimi ya bayyana cewa karancin kudi na shafar gyaran hanyoyin da kuma yaki da ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda a sassan kasar.
You must be logged in to post a comment Login