Labarai
Majalisar Dattawa ta rage kwanakin da ta sanar na zaben badi

Majalisar Dattawa ta rage kwanakin da ta sanar na zabe zuwa 300 domin kauce wa cin karo da Ibadar Azumin badi.
Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da gyaran sashe na 28 na kudirin dokar zabe ta shekarar 2026 inda ta rage adadin kwanakin sanar da zaben gama-gari daga kwanaki 360 zuwa kwanaki 300.
Rahotanni sun ce an yi wannan gyara ne domin tabbatar da cewa zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya na shekarar 2027 ba su zo daidai da watan azumin Ramadan ba.
Tun da farko majalisar ta amince da kudirin da sharadin kwanaki 360, sai dai daga bisani ta janye wancan mataki tare da mayar da kudirin gaban kwamitin majalisa domin sake duba shi.
Gyaran dai na nufin ba wa INEC karin sassauci wajen tsara ranakun zabe, tare da la’akari da yanayin addini da zamantakewa.
You must be logged in to post a comment Login