Connect with us

Labarai

Majalisar dattijai ta bayyana matsayar ta kan batun ƙirƙiro sabbin jihohi

Published

on

Majalisar dattijai ta ki amincewa da batun shawarar kirkirar sabbin jihohi.

Kwamitin majalisar kan gyaran kundin tsarin mulkin kasa na shekarar 1999 ya ce, bai yi shawarar kirkiro sabbin Jihohi 20 ba a yanzu.

A cewar kwamitin, an jawo hankalin sa kan wani rahoto da kafofin yada labarai ke yadawa cewa, kwamitin ya ba da shawarar ƙirƙirar ƙarin Jihohi 20 a Najeriya.

Kwamitin ya ce babban kuskure ne batun sake kirkiro jihohi, sai dai matukar akwai bukatar hakan to kuwa sai an bi wasu ƙa’idojin sashe na 8 na kundin tsarin Mulkin Najeriya na 1999 tare da yi masa kwaskwarima.

Cikin ƙa’idojin kuwa kwamitin ya ce, har da batun samun rinjaye da kaso biyu cikin uku na wakilan majalisar, kan batun ƙirƙirar sabbin jihohin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!