Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Ba a samu rahoton ganin watan Muharram ba – Sarkin Musulmi

Published

on

Mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar ya ayyana ranar Talata a matsayin 1 ga watan Muharram na sabuwar shekara.

Wannan ya biyo bayan rashin samun rahoton ganin wata a ranar Lahadi 29 ga watan Zul-hajj.

Sarkin musulmi ya ce, kwamitin duban wata bai samu labarin ganin wata daga kowanne bangare ba, a don haka watan Zul-hajj zai cika kwanaki 30.

Alhaji Sa’ad Abubakar yana mai cewa, sabuwar shekarar musulunci ta 1443 za ta fara daga ranar Talata 10 ga watan Agusta, a matsayin 1 ga watan Muharram 1443.

Bayanin hakan na cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addini Farfesa Sambo Wali ya fitar, tare da bukatar al’ummar musulmi su ci gaba da yiwa kasa addu’o’in zaman lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!