Connect with us

Kaduna

Majalisar Dokokin Jahar Kaduna ta mayar da rahotanin kwamatocin majalisar biyu ga ‘yan kwamatin domin sake gyara akan su

Published

on

Majalisar Dokokin Jahar Kaduna ta mayar da rahotanin kwamatocin majalisar biyu ga ‘yan kwamatin domin sake gyara akan su kafin a amince dasu.

Majalisar a zamanta na Talatar nan tun da fari ta bukaci Shugaban marasa rinjaye na majalisar Ali Kalat da ya gabatar da rahotan kwamatin sa kan kafa Hukumar koyar da sana’o’i ta Jahar wanda kudiri ne na Majalisar zartarwa.

Kazalika shima shugaban kwamatin Ilimi na majalisar Barista Muhamud Lawal Ismail ya gabatar da rahotan sa wanda dukaninsu aka mayar dasu ga kwamatocin domin sake gyare-gyare akan su, kamar yadda Barista Muhamud Lawal Ismail yayi ma wakilin mu karin haske kan yadda ta kasance a majalisar.

Majalisar dai ta baiwa kwamatocin yan kwanaki kadan na kammala gyaran domin su kuma sake dawowa da majalisar rahotanin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!