Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin jihar Kano ta aika wasikar gayyata ga gwamna Abdullahi Umar Ganduje

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da aikawa da wasikar gayyata ga gwamna Abdullahi Umar Ganduje da ya gurfana gaban kwamitin binciken wasu faifan video da ake zargin gwamnan ya karbi na goro a gobe juma’a.

Wasikar mai dauke da kwanan wata talatin da daya ga watan jiya na Oktoba, jaridar solacebase ta ruwaito cewa an karbi sakon a gidan gwamnatin Kano a jiya Laraba.

Idan za a iya tunawa a rana ita yau alhamis 25 ga watan jiya na Oktoba ne, mawallafin jaridar Daily Nigeria da ta yada faifan video wanda a cikin sa a aka yi zargin cewa gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje na karbar na goro wato Jaafar-Jaafar, ya gurfana gaban majalisar, ya kuma ba da bahasi.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!