Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta tantance shugaban hukumar tsara birane na jihar Arc. Ibrahim Yakubu Adamu da za’a naɗa a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

Arc Ibrahim Yakubu Adamu da za’a na naɗa a matsayin sabon kwamishinan yace zai ɗora akan irin ayyukan da ya saba yi a hukumar tsara birane ta jihar kano a duk inda ya tsinci kan sa domin bayar da ci gaba a faɗin jihar Kano.

Da yake amsa tambayoyi daga ƴan majalisun Arc. Ibrahim Yakubu ya jaddada mahimmancin sabunta ƙudiri na ci gaba da tsare-tsare na birane da yankunan karkara.

Ya kuma bayyana farin cikinsa da yadda Majalisar ta amince da shi, inda ya yi alƙawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke duk wani nauyi da aka ɗora masa a wannan lokacin.

Da yake jawabi Kakakin majalisar dokokin Kano Rt. Hon. Jibril Ismail Falgore, ya buƙaci wanda aka zaɓa ya ci gaba da aiki tukuru, kamar yadda ya yi aiki tukuru a hukumar tsara birane ta jihar wato KNUPDA.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!