Connect with us

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta bukaci gwamnati ta gaggauta daukar matakan tsaro a wasu yankuna sakamakon matsin lambar yan ta’adda.

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar da ta dauki matakin gaggawa kan matsalar tsaro da ke ƙara ta’azzara a Tsanyawa da Bagwai.

 

Wannan kiran ya biyo bayan kudiri na gaggawa da ‘yan majalisar da ke wakiltar yankunan suka gabatar yayin zaman da kakakin majalisar Jibril Isma’il Falgore ya jagoranta.

 

Masu gabatar da kudirin, Ali Lawan Alhassan Kiyawa da Garba Ya’u Gwarmai, sun ce matsalolin satar shanu, garkuwa da mutane da kisa sun ƙaru sosai a ‘yan kwanakin nan.

 

Majalisar ta bukaci gwamnati ta ƙara jami’an tsaro da kuma fitar da kuɗaɗen tallafi ga hukumomin da abin ya shafa, don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!