Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin Kano ta bukaci gwamnati da ta kwace sinadaran hada lemuka a kasuwannin jihar

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta umarci kwamitocinta uku da su gudanar da bincike tare da gabatar mata da rahoto kan wata annoba da ta yadu a nan Kano a baya-bayan nan sakamakon zargin shan wasu abubuwan haɗa lemo.

Kwamitin sun hada da na: harkokin lafiya da na harkokin Kasuwanci da kuma na muhalli.

Hakan ya biyo bayan ƙudurin gaggawa da ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Bunkure Muhammad Uba Gurjiya ya gabatar yayin zaman majalisar na yau talata.

Haka kuma mambobin majalisar sun buƙaci gwamnatin Kano da ta ɗauki nauyin mutanen da suka gamu da iftila’in kasancewar wasu daga cikinsu marasa galihu ne.

Da yake gabatar da ƙudurin, Muhammad Uba Gurjiya ya buƙaci da gwamnati ta bada umarnin kwace irin waɗannan sinadarai a duk inda suke tare da kara ƙaimi wajen gudanar da bincike kan ababen ci da sha da ake shigo da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!