Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Kano ta bukaci gwamnati ta gyara hanyoyi a Kura da Garun Malam da Rano

Published

on

Majalisar dokokin Kano ta bukaci gwamnatin jihar ta gaggauta kai wa al’ummar yankunan Garun Malam zuwa yada kwari da Titin zuwa Zaria dauki wajen gyara hanyarsu da tsayinta ya haura fiye da kilomita 30.

 

Dan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Kura da Garun Malam Zakariyya Alhassan, ne ya bayyana hakan a zaman majalisar na yau Talata domin ɗaukar matakin gaggawa wajen magance matsalart da ga al’ummar yankin ke fuskanta.

 

A dai zaman majalisar na yau Ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Rano Hon Ibrahim Malami Rano shi ma ya gabatar da ƙudirin gaggawa ga inda ya yi kira ga gwamnatin kano da a gyara hanyar tsohuwar kasuwa ta ƴan Barkono zuwa Gwangwan ta shiga Gobura ta hada da garin Saji.

 

Majalisar Dokokin ta jihar Kano, ta kuma sha alwashin ganin ta tura buƙatun ga gwamnati domin ɗaukar matakin gyara a kan lokaci. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!