Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin kano ta yi dokar tarar dubu 25 ga duk wanda aka kama da tofar da yawu da majina akan tituna

Published

on

Majalisar dokokin Kano ta yi dokar cin tarar naira dubu 25 ga duk wanda aka kama da tofar da yawu, majina, yin bahaya ko zubar da Shara a sha tale-tale da karkashin gadojin dake Kano.

Wannan ya biyo bayan dokar da majalisar ta Samar wadda zata gudanar da ayyukan hukumar kawata birnin Kano da Kula da wuraren shakatawa.

Da yake Karin bayani ga manema labarai, Shugaban masu rinjaye na majalisarLawan Hussaini Dala yace, ya zama wajibi gwamnati ta dauki matakan da zasu tsaftace Kano domin shigar da jihar sahun biranen duniya a fannin tsafta da cigaba.

Lawan Hussaini Dala yace, bayan tarar ta naira dubu 25, akwai Kuma sauran hukunce-hukunce da dokar ta tanada wadanda za’ayi amfani dasu wajen ladabtar da duk wanda aka samu da laifukan

Majalisar ta kuma yi karatu na biyu kan gyaran dokar hukumar kwashe Shara da tsaftar Muhalli ta Kano domin Samar da mataimakin Shugaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!