Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da ɗumi-ɗumi: Majalisar dokoki ta rushe masarautun Kano guda 5

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta rushe ɗaukacin masarautun jihar guda biyar.

Majalisar ta yi hakan ne bayan da ta amince da gyaran dokar da ta kafa masarautun guda 5 a jihar.

Gyaran dokar ya yi tanadin cewa, Duk ofisoshin da aka kafa a karkashin dokar da aka soke ya zama rusasshe.

Haka kuma duk hakimai da aka daukaka ko aka nada a karkashin dokar da aka soke za su koma kan mukamansu na baya.

Shugaban masu rinjaye kuma memba mai wakiltar Dala a zauren Alhaji Lawan Hussaini Chediyar ƴan Gurasa, ne ya dauki nauyin gabatar da ƙudurin gyaran dokokin.

Yayin ganawarsa da manema labarai, shugaban masu rinjayen ya ce, a yanzu babu sarki a Kano sai wanda gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya naɗa.

Haka kuma ya ƙara da cewa, cikin gyaran da aka yi an mayar da jihar Kano mai masarauta guda ɗaya, sai dai, nan gaba za a ƙirƙiri wasu masarautun masu Daraja ta biyu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!