Labarai
Majalisar Wakilai ta yi sammaci ga Ministocin Kuɗi da na Noma

Majalisar Wakilai kasar nan ta yi sammacin Ministocin Kudi da na Noma da Babban Odita Janar na kasa don su yi bayani kan kashe kudaden da aka fitar don shirye-shiryen noma tsakanin 2015 da 2025.
Kwamitin wucin gadi na Majalisar Wakilai da ke binciken Tallafin Noma, ne ya bayar da sammacin a wani zaman sauraron ra’ayin jama’a da aka yi a Abuja .
Kwamitin ya yanke shawarar cewa jami’an ko wakilan da aka nada su bayyana a gaban kwamitin a ranar 3 ga Fabrairu mai kamawa.
‘Kwamitin yayi gargadin cewa rashin cika gayyatar zai jawo takunkumin majalisa bisa ga ikon majalisar dokokin ta kasa.
You must be logged in to post a comment Login