Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Malam Ibrahim Khalil ya zama shugaban malaman Arewa maso yamma

Published

on

Gamayyar malaman addinin musulunci sun zaɓi Malam Ibrahim Khalil a matsayin shugaban majalisar malamai shiyyar Arewa maso yamma.

Zaɓen na sa ya biyo bayan taron da gamayyar malaman yankin suka gudanar a birnin Katsina aranakun Jumu’a da Asabar 16 da 17 ga watan Oktoban da muke ciki.

Kafin wannan zaɓe dai, Sheikh Ibrahim Khalil shi ne shugaban majalisar malamai ta ƙasa reshen jihar Kano.

A yayin taron an kuma zaɓi shugaban majalisar malamai na jihar Jigawa Khadi Bashir Umar Birnin Kudu a matsayin babban sakataren majalisar malaman na yankin Arewa maso yamma.

Tuni majalisar malamai ta Kano ta aike da saƙon taya murna ga waɗanda aka zaɓa ta bakin sakataren majalisar Malam Ibrahim Tofa, yana mai an yi zaɓen bisa cancanta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!