Labarai
Mali za ta saki ƴan ta’adda fiye da 100 saboda samun damar kai fetur biranen da ke ƙarƙashin ƴan ta’adda

Gwamnatin kasar Mali ta amince ta sakin ƴanta’adda sama da 100 saboda samun damar kai man fetur a wasu biranen da ke ƙarƙashin ƴan ta’adda.
Tun cikin watan Satumbar bara ne dai, ƙungiyar ta masu ikrarin jihadi da ta samo asali daga Al-Qaeda ta fara kai hari kan tawagar tankokin mai a Bamako, babban birnin ƙasar.
A cewar wani jami’in gwamnati kuma mazaunin Bamako, an saki ƴan ta’adda sama da 100 ne, a matsayin musayar buɗe hanyoyin da manyan motocin dakon mai da sauran kayayyaki za su wuce wanɗanda masu ikrarin jihadin suka kawo tsaikon wucewar ta su.
You must be logged in to post a comment Login