Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Mambobin kungiyar JUPTI sun tsunduma yajin aiki bisa rashin albashin watanni 5

Published

on

Hadaddiyar kungiyar malaman manyan makarantu ta jihar Plateau JUPTI ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani saboda rashin biyan albashin malamai na watanni biyar.

Rahotanni sun bayyana cewar, kungiyar ta dauki wannan matakin ne biyo bayan wata wasika da uwar kungiyar ta aikewa gwamna jihar mai kwana wata 23 ga watan jiya dake dauke da sa hannun hadin gwiwa na shugaban Mr Paul Dakogol da kuma sakataren ta Ayum Solomon suka sanya wa hannu.

Amma kuma a karshen shekara ta 2016, gwamnatin jihar ta yi alkawarin zata biya malaman dukkanin hakokin su.

Haka zalika rahotanni sun bayyana cewar, an hana dalibai shiga harabar kwalejin kimiya da fasaha ta jihar da sauran manyan makarantu, saboda matakin da kungiyar ta dauka da tsunduma yajin aiki.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!