Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Antoni janar da wasu manyan gwamnatin na kasar Burtaniya don bude shari’ar Kamfanin P&ID

Published

on

Attorney Janar na kasa kuma Ministan shari’a Abubakar Malami da sufeto Janar na ‘yan sandan kasar nan Muhammed Adamu da gwamnan babban bankin kasa CBN Godwin Emefiele, sun tafi kasar Burtaniya domin sake bude sabuwar shari’a da kamfanin P&ID wanda wata kotun kasuwanci ta Burtaniya ta ba ta umarnin kwace kadarorin kasar nan da suka kai darajar dala biliyan tara da miliyan dari shida.

Haka zalika Ministan yada labarai Alhaji Lai Muhammed da kuma mai rikon mukamin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC Ibrahim Magu, suna cikin tawagar da su ka tafi burtaniya.

A dai watan jiya na Agusta ne wata kotun kasuwanci da ke Burtaniya ta yanke hukuncin cewa kamfanin P&ID yana da hurumin kwace kadarorin kasar nan a duk inda ya same su da darajarsu suka kai sama da dala biliyan tara sakamakon zargin hukumomin kasar nan da karya kai’don kwangilar harkar gas.

Bayan yanke hukuncin ne a watan jiya ministar kudi, kasafi da tsare-tsare, Zainab Ahmed , ta bayyana hukuncin a matsayin marar adalci kuma kasar nan ba za ta amince da hakan ba

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!