Labarai
Matar da ta haifi jarirai 5 a Kano ta rasu

An gudanar da janaizar Marigayi Hafsat Yusif, wadda ta haifi jarirai biyar jiya Laraba a Asibitin kwararu na Murtala Muhammad a nan Kano.
Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano ta ce, mahaifiyar yan biyar din Malama Hafsat Yusif, ta rasu ne sakamakon zubar jini duk da kokarin da jami’an lafiya suka yi wajen ceto rayuwarta kamar yadda jami’in yada labarai na ma’aikatar Nabulisi Abubakar Kofar Naisa, ya shaida wa wakilinmu Abba Isah Muhammad.
Malam Salisu Nafi’u, Shi ne mijin marigayya ya bayyana cewar, yanzu haka sun gudanar da jana’izar marigayar a Unguwar hotoro Ladanai da ke nan Kano.
A zantawar marigayya Hafsat Yusif, da manema labarai a jiya Laraba bayan haihuwarta, ta bayana wasu cikin burinta idan Allah ya rayata da yayan nata, inda ta ce, tana so su samu damar yin karatu mai zurfi.
You must be logged in to post a comment Login