Connect with us

Labarai

Mazauna Kontagora da wasu yankuna a Jihar Neja sun gudanar da addu’o’in neman ɗaukin Ubangiji kan hare-haren ‘Yan bindiga

Published

on

Mazauna yankunan  Neja ta Arewa sun gudanar da taron addu’a ta musamman a filin Idin Kontagora, hedikwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon Allah kan yawan hare-haren ‘yan bindiga da suka addabi al’ummomin manoma a yankin.

 

Yankunan da abin ya fi shafa sun haɗa da Magama, Mariga, Rijau, Borgu, Kontagora da Mashegu, inda hare-haren suka ƙaru a makonni kalilan da suka gabata, lamarin da ya tilasta wa daruruwan mazauna, musamman mata da yara, barin gidajensu domin tsira da rayukansu.

 

Wannan matsanancin hali ne ya sa jama’ar yankin suka nemi mafita ta hanyar addu’a domin neman sauƙi daga wannan matsalar tsaro da ta daɗe tana damunsu.

 

Wani daga cikin mutanen da suka rasa matsugunansu, wanda bai so a bayyana sunansa ba, ya shaida wa Daily Trust cewa ɗaruruwan musulmi daga yankunan da abin ya shafa – ciki har da Kontagora, Mashegu, Rijau da Magama – sun halarci taron addu’a.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!