Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Mbappe ya tafi jinyar rauni na mako uku

Published

on

Dan wasan gaban kungiyar Kwallon kafa ta Paris Saint German (PSG), ta bayyana cewar dan wasanta Kylian Mbappe zai shafe sati uku yana jinyar raunin da ya samu.

Tafiya jinyar da dan wasan zai yi , ta sa ba zai samu damar buga wasan da tawagar sa zatayi da da Atlanta ta kasar Italiya ba a gasar cin kofin Zakarun Turai na Champions league , ranar 12 ga watan Augusta, a wasan dab da na kusa da na karshe wato Quarter Final.

Dan wasan ya samu rauni a idon sawun sa (Ankle ) bayan da sukayi arangama da dan wasan Saint Etienne Perin, a wasan karshe na Coupe de France , da PSG ta samu nasara da ci 1 da nema.

Tafiya, jinyar dan wasan ta kawo tasgaro a kokarin da kungiyar take na daukar kofin Zakarun turai , wanda yake daga gaba -gaba a burin kungiyar .

Mbappe , ya zura kwallaye 30 a gasa daban -daban daya bugawa PSG a Bana, kafin a baiwa tawagar nasarar lashe kofin kasar Faransa na Ligue 1, bayan dakatar da gasar sakamakon Annobar Corona.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!