Labarai
IMF: Bashin wajen Najeriya zai kai Dala Biliyan 72.6 bayan zaben 2027

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya yi hasashen cewa bashin wajen Najeriya zai karu zuwa dala biliyan 72.6 nan da shekarar 2027, daga dala biliyan 51.9 da ake da shi a shekarar 2025. IMF ya danganta yiwuwar karin bashin da bukatun kashe kudi da kuma matsin tattalin arziki gabanin babban zaben kasar.
Rahoton ya bayyana cewa karin talauci, matsalar tsadar abinci da bukatun gwamnati na iya kara gibin kasafin kudi, lamarin da zai sa Najeriya ta ci gaba da neman karin lamuni daga kasashen waje. Haka kuma, IMF ya gargadi gwamnati kan wasu tsare-tsaren karbar bashi da ka iya jefa tattalin arzikin kasar cikin hadari.
Duk da haka, IMF ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta aiwatar sun kara wa tattalin arzikin kasar karfi, tare da hasashen cewa GDP na Najeriya zai bunkasa da kashi 4.1 cikin dari a 2026 da kuma kashi 4.3 cikin dari a 2027.
You must be logged in to post a comment Login