Connect with us

Ƙetare

Mojtaba Khamenei ya zama sabon jagoran addinin ƙasar Iran

Published

on

Mojtaba Khamenei ya zama sabon jagoran addinin ƙasar Iran, bayan da majalisar ƙwararrun ƙasar ta zaɓe shi domin ya gaji mahaifinsa Ayatollah Ali Khamenei.

Gidan talabijin na gwamnatin Iran ne ya sanar da hakan, inda aka ce duk da halin yaƙi da kuma hare-haren da aka kai ofisoshin majalisar, wanda ya yi sanadin mutuwar wasu mambobinta da jami’an tsaro, majalisar ba ta dakata ba wajen gudanar da zaɓen sabon jagoran tsarin Musulunci.

Sanarwar ta ce majalisar ta tabbatar da naɗin Mojtaba Khamenei a matsayin jagoran addinin ƙasar, lamarin da ya sa ya zama jagora na uku a tarihin Iran, kuma na farko da ya gaji mahaifinsa.

Rahotanni sun ce an daɗe ana hasashen Mojtaba zai gaji mahaifinsa tun bayan da aka kashe Ali Khamenei a harin da Amurka da Isra’ila suka kai.

An haifi Mojtaba Khamenei a ranar 8 ga watan Satumban 1969 a birnin Mashhad, kuma shi ne na biyu cikin ’ya’yan Ali Khamenei shida.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!