Connect with us

Labarai

Mun dakatar da shirin fara karɓar harajin kaso 15 cikin 100 kan fetur- NMDPRA

Published

on

Hukumar kula da harkokin man fetur ta Najeriya NMDPRA ta ce, ta dakatar da shirin fara karɓar harajin kaso 15 cikin 100 kan albarkatun man fetur ɗin da ake shigaar da su Najeriya daga ƙasashen ketare.

Mai magana da yawun hukumar ta NMDPRA George Ene-Ita, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar yau Alhamis inda ya bukaci al’umma da su daina fargaba.

A baya dai a  ranar 29 ga watan Oktoba shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya amince da saka harajin kan man fetur da Man Dizel, wanda zai ƙara farashin man da ake saukewa a defo-defo, kuma ɗaya daga cikin manufarta shi ne ƙarfafa matatun mai na cikin gida.

Gwamnatin tarayya ta ce da ta tsara fara aiki da harajin ne  daga ranar 21 ga watan Nuwamban nan, kafin matakin tsaida amfani dashi da  ta sanar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!