Connect with us

ilimi

Muna da ƙarancin kayan koyo da koyarwa a makarantu – NUT

Published

on

Kungiyar malamai ta kasa rashen jihar Kano NUT ta bayyana cewa baban Ƙalubalen da suke fuskanta bai wuce na rashin kayan koyo da koyarwa.

Kazalika ƙungiyar ta kuma ce, akwai cunkoso a azuzuwan makarantu musamman ma a jihar Kano.

Shugaban kungiyar Muhammad Abubakar ne ya bayyana hakan a wani bangare na bikin ranar malamai ta duniya.

Ya ce “Tun bayyan da gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa ilimi kyauta kuma dole ga ɗaliban Kano, ana fuskantar yawan ɗalibai da kuma rashin isassun kayan koyo da koyarwa a makarantu”.

Kungiyar ta kuma buƙaci gwamnati ta da bai wa malamai a makarantu horo na musamman, kasancewar da dama daga cikin malaman ba su da ƙwarewar koyarwa.

Taken bikin ranar malamai ta duniya a bana shi ne Malamai ke da haƙƙin kawo gyara a harkokin ilimi.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!