Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta fara biyan mu bashin da muke bin ta – NARD

Published

on

Ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta ƙasa reshen jihar Kano ta ce gwamnatin tarayya ta fara biyan su kuɗaɗen da suke bin ta ba shi.

Ƙungiyar reshen asibitin Aminu Kano ce ta bayyana hakan ta bakin jami’in walwalar ƙungiyar Dakta Haruna Yakubu a zantawar sa da Freedom Radio ta cikin Labaran Mu leƙa mu gano.

“A yanzu gwamnatin tarayya ta fara biyan wasu daga cikin mu kuɗaɗen su na albashi da suke bi bashi, kuma tana ci gaba da tantancewa don kammala biya” in ji Dakta Haruna.

Likitan ya ce, “Mun cimma matsaya da gwamnatin tarayya kan cewa za ta janye ƙarar da ta shigar da mu gaban kotun ɗa’ar ma’aikata, kuma za ta mayar da dukkanin jami’an lafiya tsarin biyan albashi na IPPIS”.

Dakta Haruna Yakubu ya kuma ce, tsawon wata biyu kenan gwamnatin tarayya ba ta ba su albashi ba, sakamakon ƙoƙarin ta na cika alƙawarin da ta ɗauka na cewa ba za ta bada albashi ga ma’aikatan da suke yajin aiki ba.

“Mun sha wahala matuƙa da rashin albashi, domin kuwa mafi yawan mu ba mu da wani aiki da muka dogara da shi sai aikin kula da lafiya” a cewar Dakta Haruna.

Wannan dai ya biyo bayan janye yajin aikin da ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta yi a ranar Litinin, wanda ta shafe sama da wata biyu tana gudanarwa sakamakon zargin cewa gwamnati ta ƙi biya musu buƙatun su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!