Connect with us

ilimi

Muna gab da kammala Sauya tsarin Manhajar karatun Sakandare- Ministan Ilimi

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce tana gab da kammala Sauya tsarin Manhajar Karatun Makarantun Sakandare.

 

Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan a taron ƙasa da ƙasa na ƙungiyar masu tsara manhajar ilimi ta Afirka, wanda aka gudanar a Abuja.

 

Ya kuma ce tuni an kammala kuma an amince da sabuwar manhajar karatun firamare da kuma sakandare na ƙasa (daga aji ɗaya zuwa na uku). Sai ya ce yanzu ana kan matakin ƙarshe na sauya manhajar matakin makarantun sakandare.

 

Ministan, wanda mataimakiyar sa, Farfesa Suwaiba Ahmad ta wakilta, ya tabbatar da cewa sabon tsarin makarantun sakandare da ake shirin ƙaddamarwa zai yi daidai da ƙa’idojin ilimi na duniya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!