Connect with us

Labarai

Muna samun nasara kan ‘yan ta’adda – Sojin Najeriya

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta tabbatar da samun nasara a ci gaba da kai farmaki da take yi kan yan ta’adda a sassan kasar nan

 

A cikin wata sanarwa da Shelkwatar sojin Kasa ta fitar a shafinta na Facebook a daren jiya Talata  ta ce cikin awanni 72 da suka gabata dakarunta sun kashe kusan yan ta’addan 47 a hare hare daban daban a Arewa maso yamma da Arewa ta tsakiya.

 

Haka zalika sun ce  an Kama mutane 19 da ake zargi da aikata laifuka sannan an ceto sama da mutane 30 da aka sace a yayin sumamen.

 

Sojojin sun  kwato tarin makamai da harsasai da kayan aiki bayan gudanar da hadin gwiwar hare haren Kasa da na sama bisa samun bayanan sirri.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!