Connect with us

Labarai

Mutanen da suka rasu a hatsarin jirgin ruwan Neja sun karu zuwa 60

Published

on

Hukumar bayar da agajin  gaggawa ta jihar Neja  ta ce, zuwa yanzu adadin mutanen da suka rasu sakamakon hatsarin jirgin  ruwan da ya afku ya kai zuwa 60.

 

 A baya dai, rahotanni sun tabbatar da cewa jirgin ruwan wanda ke ɗauke da fasinjoji 90 waɗanda ya ɗauka daga mazaɓar Tugan Sule, da ke yankin ƙaramar hukumar Borgu ta jihar, ya yi hatsari.

 

Bayan aukuwar hatsarin kuma, a ranar litinin ɗin da ta gabata hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja, ta bakin shugabanta, Abdullahi Baba Arah, ta tabbatar da samun gawarwakin mutum 29 daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su.

 

Kamfanin dillancin labarai na Reuters, ya rawaito cewa, an ƙara samun gawarwakin mutane inda adadin ya ƙaru zuwa 60.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!