Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NEMA ta tabbatar da mutuwar jami’an gwamnati 2 a hatsarin Lagos

Published

on

Wani Jirgin kasa a Jihar Lagos da ya yi taho mu gama da wata motar Bas a kan hanyarsa da ke Ikeja babban birnin jihar.

Rahotonni sun bayyana cewa, ana fargabar rasuwar ma’aikatan gwamnatin jihar biyu yayin da wasu kuma da dama suka jikkata sakamakon taho mu gama din da jirgin kasan ya yi da motar da safiyar yau Alhamis.

Motar na dauke da wasu ma’aikatan gwamnati ne, wandada suke kan hanyarsa ta zuwa wurin aiki inda a kokarin da motar ta yi na tsallaka layin dogon ne aka samu afkuwar iftila’in dai-dai lokacin da jirgin ke wucewa ta wurin.

Mai magana da yawun hukumar bayar da agajin gaggawa ta NIjeriya NEMA Ibrahim Farinloye, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, an gano gawarwakin ma’aikatan gwamnati mata biyu, an kuma kwashe wadanda suka jikkata da dama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!