Connect with us

Labarai

Na amince da umarnin kotu na dakatar da muƙabala – Ganduje

Published

on

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce, zai yi biyayya ga umarnin kotu na dakatar da shirin Muƙabalar malamai.

Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin Kwamishinan shari’a na jihar Barista Musa Abdullahi Lawal.

Kwamishinan ya ce, wannan Gwamnatin ba ta karya umarnin kotu, saboda haka za ta yi biyayya da umarnin musamman ganin kotun tana da hurumin bayar da shi.

Ya ci gaba da cewa, ai ba daidai ba ne a ce kotu ta bai wa Gwamnatin umarni kuma ta ƙi ba, a don haka yanzu babu batun zaman muƙabala ranar Lahadi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!