Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wata Sabuwa: Malam Abduljabbar ya yi watsi da dakatar da muƙabala

Published

on

Malamin nan Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara ya yi watsi da shirin dakatar da muƙabala da kotu ta bada umarnin.

Malam Kabara ya bayyana hakan ne, ta bakin lauyan sa Barista Rabi’u Shu’aibu Abdullahi.

Lauyan ya ce, su ba su samu umarnin kotun ba sai dai kawai a kafafen yaɗa labarai.

Labarai masu alaka:

Janye Muƙabala: Da alƙalin da lauyan su shirya abin da za su faɗa wa Allah – Martanin Dr. R/Lemo

Na amince da umarnin kotu na dakatar da muƙabala – Ganduje

Ya ci gaba da cewa, ko a baya da kotun ta bada umarnin dakatar da Malam Abduljabbar daga karatu ba a sanar da su ba, sai dai kawai sun gani a kafafen sada zumunta.

“Idan mutane suka lura da odar kotun ko sunan Sheikh Abduljabbar ba bu a jiki, kuma ba a kai masa takardar cewa za a zauna a kotu ba”.

Ya ƙara da cewa, saboda haka su ba sa cikin waɗanda ake yin shari’ar da su a gaban kotun, kuma har yanzu suna nan a shirye domin zuwa muƙabala ranar 7 ga wata kamar yadda gwamnati ta ba su a rubuce.

Wannan dai na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan da wata kotun majistiri da ke Kano ta bada umarnin dakatar da Gwamnatin Kano daga shirin muƙabalar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!