Connect with us

Labarai

Najeriya na rasa fiye da Dala biliyan 56 duk shekara- Kashim Shettima

Published

on

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cewa Najeriya ta na rasa fiye da dala biliyan hamsin da shida a duk shekara sakamakon matsalar rashin abinci mai gina jiki.

Shettima ya ce wannan matsala tana dakile ci gaban ƙasa, tana ƙara yawaitar talauci, tare da lalata ƙwarewa da damar da ‘yan ƙasa za su iya amfani da ita wajen raya tattalin arzikin ƙasa.

Ya kara da cewa, idan aka kula da batun abinci mai gina jiki da muhimmanci, hakan zai taimaka wajen inganta lafiya, rage talauci, da kuma gina ƙasa mai ƙarfi da ci gaba.

Kashim Shettima ya yi wannan bayani ne yayin wani taro na musamman da aka shirya domin tattauna hanyoyin magance matsalar rashin abinci mai gina jiki a Najeriya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!