Connect with us

Labarai

NANS ta gargaɗi ƙungiyar NUPENG kan sukar matatar Mai Dangote

Published

on

Kungiyar ɗaliban Najeriya NANS, ta gargadi ƙungiyar masu dakon man fetur ta NUPENG kan ta daina sukar kokarin da matatar man fetur ta Dangote ke yi wajen magance matsalolin fetur da tsadar sa da ake fuskanta.

Shugaban kungiyar na Olushola Oladoja, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai yau Juma’a a Abuja.

Ya kuma ce matatar ta Dangote na kokarin fitar da ‘yan Najeriya miliyan 200 daga kangin da suke ciki.

Oladoja ya ƙara da cewa, matatar mai ta Dangote, wadda ke da karfin tace gangar mai har 650,000 a kowace rana, ta zama wata babbar dama ga tattalin arzikin ƙasar, domin ta samar da wadatar man fetur ga cikin gida da kuma damar fitarwa zuwa ƙasashen ƙetare.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!