Connect with us

Labarai

NBA ta yi Allah-wadai da zargin jami’an DSS na sace wata yarinya a Jigawa

Published

on

Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Jigawa ta yi Allawadai da zargin da ake yiwa wani jami’in hukumar DSS na sace wata yarinya yar asalin garin Hadeja tsawon shekara biyu tare da canza mata addini.

 

Shugaban kungiyar a jihar Barista Hamza Garba Umar ya shaidawa Freedom Radio cewa kungiyar su za ta tabbatar da an yi adalci a wannan shari’a da zarar an kamo wadda ake zargin.

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta bakin mai magana da yawunta SP Lawan Shisu Adam ya tabbatarwa Freedom Radio cewa sun karbi umarni daga wata Kotun majistare dake Hadeja na kamo wadda ake zargin tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!