Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

NEMA:gwamnatin tarayya ta kai dauki ga al’ummar jihohin Adamawa da Taraba

Published

on

Hukumar agajin gaggawa ta kasa NEMA ta bukaci gwamnatin tarraya da ta kai dauki ga al’ummar jihohin Adamawa da Taraba, sakamakon rikicin ‘yan-tada kayar baya da rikicin kabilanci.

Babban darakta na hukumar Akube Iyawu ne ya bayyana haka, yayin zantawa da manema labarai, a babban birnin Yola na jihar Adamawa.

Akube Iyawu ya kuma ce, sun zo Jihar ne don ganiwa idanun su barnar da jihohin biyu suka samu sakamakon tashe-tahsen hankalin a sassan Jihohin.

Akube Iyawu ya kuma ce, al’ummar jihohin na bukatar agajin don kuwa yawancin su, sun rasa dokiyoyinsu da dama, hadi da matsugun-nansu  baya ga rashin zaman lafiya da ke adabar jihohin

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!