Connect with us

Labarai

NGF ta bukaci jagororin Plateau su dauki matakan dakatar da kashe-kashe a jihar

Published

on

Kungiyar Gwamnonin Najeriya, ta buƙaci jagororin jihar Plateau da su haɗa kan al’ummar jihar domin dakatar da kashe-kashen mutane da ake yawan samu.

Shugaban ƙungiyar kuma gwamnan jihar Kwara Abdulrahman Abdulrazaq, ne ya bukaci hakan da yammcin ranar Alhamis lokacin da ya kai ziyarar jaje jihar.

Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq, ya kuma bukaci masu fada aji da duk masu ruwa da tsaki a jihar da su haɗa hannu waje guda don dawo da zaman lafiya a jihar

Rahotanni sun  bayyana cewa fiye da mutune  100 aka kashe cikin makonni biyu da suka gabata, lokacin da wasu mahara suka kai hari wasu garuruwa da ke yankin ƙananan hukumomin Bokkos da Bassa a jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!