Connect with us

Labarai

NLC ta gargaɗi Gwamnatin tarayya kan yajin aikin ASUU

Published

on

Kungiyar Ƙwadago ta kasa NLC ta gargaɗi gwamnatin tarayya kan ta daina barazanar yin amfani da manufar “ba aiki, ba albashi” kan yajin aikin kungiyar malaman jami’o’imalaman jami’a ASUU.

Shugaban kungiyar ta NLC Joe Ajaero ne ya bayyana hakan a zantawarsada manema labarai.

Ajaero ya ce, gwamnati ta yi amfani da wa’adin makonni biyu da ASUU ta bayar wajen warware matsalolin da ke tsakaninsu, maimakon tsoratar da malamai. Ya bayyana cewa yajin aikin ASUU ba na malaman jami’a kaɗai ba ne, amma gwagwarmaya ce don kare makomar ilimin jama’a a Najeriya.

Ya ƙara da cewa wannan barazana ta “ba aiki, ba albashi” tana ƙara nuna bambancin tsakanin ‘ya’yan talakawa da na masu kuɗi da ke karatu a ƙasashen waje.

NLC ta ce idan bayan makonni biyu gwamnati ta kasa warware matsalar, za ta haɗa kai da ASUU da sauran ƙungiyoyin ma’aikata don tsayar da tattalin arzikin ƙasar, domin kare ilimin jama’a da tabbatar da adalci ga malamai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!