Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Yajin aiki: ASUU ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makwanni 3

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa ASUU ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makonni uku kan ta fara aiwatar da yarjejeniyar da suka suka cimma ko kuma ta tsunduma yajin aiki.

Shugaban ƙungiyar Farfesa Emmanuel Osodoke ne ya sanar da hakan bayan kammala taron shugabannin ƙungiyar na kwanaki biyu a jami’ar birnin tarayya Abuja.

Farfesa Osodoke ya ce a baya can sun janye yajin aikin da suka ƙuduri aniyar shiga bayan alƙawuran da gwamnatin tarayya ta yi na aiwatar da yarjejeniyar da suka cimma.

Sai dai a yanzu ba su da mafita fa ce shiga yajin aikin da zarar makonni ukun sun cika ba tare da samun biyan buƙata ba.

A bara ne dai ƙungiyar ta gudanar da yajin aikin watanni tara, don nuna rashin jin daɗi kan kin biya mata buƙatunta da gwamnatin tarayya ta yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!