Connect with us

Kasuwanci

NPA ta bukaci masu son fitar da kayayyaki su rika ziyartar shafinta don samun bayanai

Published

on

Hukumar kula da tashoshin jiragen ruwan kasar nan NPA ta ce damar makin da Najeriya ke da su a birnin tarayya Abuja na bunkasa harkokin Noma da Masana’antu sun zama ginshiƙi wajen ƙarfafa manufar gwamnatin tarayya ta bunƙasa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga ba tare da yin la’akari da arzikin man fetur ba.

Shugaban Hukumar Dakta Abubakar Dantsoho, ne ya bayyana hakan, yayin bikin baje kolin kasuwanci na kasa da kasa da ke gudana a Abuja da hukumar ta NPA ta shirya.

Dantsoho ya ce hukumar ta samar da Cibiyoyin Sarrafa Kayayyakin Fitarwa domin sauƙaƙa duk wasu matakai na fitar da kayayyaki daga kasar nan, ta yadda za a gujewa tsaikon da ake samu a kasuwannin Duniya.

Dantsoho ya ƙara da cewa hukumar tana aiki kan tsarin Ports Community System (PCS) da kuma National Single Window (NSW) da zai haɗa duk masu ruwa da tsaki a fannin kasuwanci a rukuni daya da yai dai-dai da zamani, don magance jinkiri da kawar da matsalolin kasuwanci.

Hukumar tashoshin jiragen ruwan ta kuma roƙi ‘yan kasuwa da masu saka hannun jari kan su yi amfani da sauƙaƙan hanyoyin fitar da kaya, tare da ziyartar shafin hukumar a kan www.nigerianports.gov.ng domin samun dukkan bayanan da ake buƙata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!