Connect with us

Labarai

PDP ta yi soka kan sunayen da Tinubu ya tura Majalisa don nada su jakadu

Published

on

Jam’iyyar adawa ta PDP, ta soki jerin sunayen waɗanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tura wa Majalisar Dattawa domin nada su matsayin jakadu, inda ta bayyana jerin sunayen a matsayin abin kunya da kuma takaici.

A cewar jam’iyyar, yawancin waɗanda aka zaba suna laifin da suka shafi rashi gaskiya da almundahana. Daga cikin sunayen da suka jawo ce-ce-ku-ce akwai tsohon Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu.

PDP ta ce nada shi a wannan lokaci na iya zama ladan zaben da ya bawa shugaban kasa Tinubu nasara, kuma hakan na iya zama barazana ga zaben shekarar 2027.

Jam’iyyar ta bukaci Shugaba Tinubu ya janye jerin gaba ɗaya, ya kuma sake gabatar da mutanen da ke da nagarta, kima, da abin alfahari da za su kare martabar Najeriya a fagen diplomasiyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!