Connect with us

Labarai

Jam’iyyar PDP ta yi watsi da umarnin kotu

Published

on

Jam’iyyar PDP ƙarƙashin shugabancin Kabiru Tanimu Turaki ta yi watsi da hukuncin da wata babbar kotun tarayya ta bayar wanda ya soke babban taron da ta gudanar a birnin Ibadan na 15 ga watan Nuwamban 2025.

 

Shugaban jam’iyyar, wanda aka zaɓa a lokacin babban taron na Ibadan, Kabiru Tanimu Turaki ya shaidawa manema labarai a birnin Abuja cewa za su bi matakan shari’a domin ƙwatar haƙƙinsu.

 

Ya zargi kotun da tafka kuskure a hukuncin da ta bayar, wanda ya fitar da buƙatar da babu wani ɓangare da ya nemi a biya masa, daga cikin masu jayayya da juna.

 

A ranar Juma’a, 30 ga watan Janairun 2026 wata babbar kotun tarayya a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, ta rusa shugabancin jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!