Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin nasarar yi wa Sanata Dino Melaye kiranye ba zai gurgunta siyasata ba-Gwamna Yahaya Bello

Published

on

Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello ya ce rashin nasarar yi wa Sanata Dino Melaye kiranye ba zai taba gurgunta masa siyasa ba, in ji mai magana da yawun gwamnan na Kogi Petra Onyegbule.

Yunkurin kiranyen na dan-majalisar Dattijan Kogi ta Yamma Sanata Dino Melaye ya gaza cimma nasara ne a ranar Asabar din da ta gabata bayan da kashi biyar ne kadai na masu kada kuri’a suka halarci kiranyen sbanin yadda doka ta bukaci har sai kashi 51 sun amince sannan kiranyen zai tabbata.

Masharhanta na ganin cewa kiranyen ya samu tasgaro sakamakon yadda gwamnatin Jihar ta Kogi ta ki biyan ma’aikata albashin wata-da-watanni, duk da cewa gwamna Yahaya Bello ya bayyana al’amarin a matsayin yunkurin kakkabe ma’aikatan bogi daga cikin ma’aikatan gwamnatin Jihar.

Dino Melaye ya zama dan-majalisar Wakilai a shekarar 2007 karkashin inuwar jam’iyyar PDP sai dai daga bisani ya sauya sheka zuwa jam’iyya mai mulki ta APC inda aka zabe shi a matsayin Sanata a shekarar 2015.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!