Connect with us

Labarai

Rundunar Sojin kasar nan ta hallaka  aƙalla ‘yan ta’adda 60 a Borno

Published

on

Rundunar Sojin kasar nan  ƙarƙashin Operation Hadin Kai sun hallaka  aƙalla ‘yan ta’adda 60 a wani gagarumin farmaki da suka kai wa Boko Haram a garin Bita da ke jihar Borno. 

Bayanin nasarar dai na kunshe  ne a cikin wani sako da rundunar sojin kasar nan ta wallafa a shafin ta na X.

Rundunar ta ce  farmakin wanda ya haɗa da hare-haren ƙasa da na sama, an gudanar da shi da tsakar dare, wanda ya janyo mummunan hasara ga ‘yan ta’addan.

Harin ya biyo bayan bude wuta da ‘yan ta’addar suka yi, inda sojoji suka mayar da martani, tare da samun taimakon jiragen yakin  A-29 Super Tucano da Dragon, waɗanda suka yi luguden wuta kan ‘yan ta’addan. 

Bayan artabu mai tsanani da ya ɗauki kusan sa’o’i biyu da rabi, rahotanni sun tabbatar da cewa an kashe aƙalla ‘yan ta’adda 60, tare da  lalata motocin su  biyu da ke ɗauke da bindigogi. 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!