Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar sojin kasar nan ta kai samage ofishin jaridar Daily trust da ke Maiduguri

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta ce ta kai samame ofisoshin jaridar jaridar Daily Trust da ke Maiduguri da Abuja ne da nufin gayyatar ‘yan jaridun kamfanin wadanda ke da alhakin ruwaito wani labari da ya fallasa dabaru da kuma tsare-tsaren ayyukan dakarun operation lafiya dole a jihar Borno.

Mai magana da yawun rundunar burgediya janar Sani Usman Kuka Sheka ne ya bayyana haka ga manema labarai ta cikin wata sanarwa da ya fitar jiya.

A cewar sanarwar fallasa dabaru da kuma tsare-tsaren ayyukan soji laifine babba da ke barazanar ga tsaron kasar nan.

Sanarawar ta kuma ce sojojin sun je ofishin jaridar ne da nufin gayyatar ‘yan jaridar da suka ruwaito labarin.

Burgediya janar Sani Usman Kuka Sheka ya kuma ce, rundunar za ta ci gaba da bincike kuma duk wadanda aka samu suna da hannu wajen fitar da bayanai na sojin za a dauki tsastsauran mataki a kansu.

A jiya lahadi ne dai jaridar Daily Trust ta wallafa wani labari kan shirye-shiryen da dakarun operation lafiya dole ke yi na kakkabe mayakan Boko-haram daga yankin Baga da wasu yankuna da ke makwabtaka da wajen.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!