Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar ‘Yan sanda ta kubutar da ‘Yan Afrika ta Kudu biyu da aka sace su a Kaduna

Published

on

Rundunar ‘Yan sandan Najeriya ta ce ta kubutar da wasu ‘Yan kasar Afrika ta Kudu biyu da aka sace su a wani wurin aikin hakar ma’adinai cikin kauyen Maidaro a jihar Kaduna.

Wata sanarwa da mai Magana da yawun rundunar ‘yan sandan Jimoh Mashood ya fitar, ta ce sai da jami’an tsaro suka yi amfani da jirgi mai saukar Ungulu da wasu ‘yan sanda na musamman kafin cimma sako mutanen guda biyu.

Mutanen da aka kubutar sun hada da Thomas Arnold Pearce da Mista Hendrik Gideon bayan sace su a ranar Talata 23 ga watan Janairun da muke ciki  a kauyen Maidaro.

Sanarwar kuma ta ce an sako mutanen ne a jiya Asabar  ba tare da wani rauni a jikin su ba.

Sai dai rundunar ‘yan sandan ba ta yi bayani ba ko sai da aka biya kudin fansa kafin a sake su.

Al’amarin dai na zuwa ne kasa da mako guda bayan kubutar da wasu turawa ‘yan Amurka biyu da kuma ‘yan Canada biyu da aka sace a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!